Daga Khalifa Abdullahi MaiKano
A ranar Laraba ne kotun koli ta dakatar da matakin da gwamnatin tarayya ta dauka na dakatar da amfani da tsofaffin takardun kudi na naira daga ranar 10 ga watan Fabrairun 2023.
Wani kwamiti mai mutane bakwai karkashin jagorancin mai shari’a John Okoro, ya dakatar da matakin da gwamnatin tarayya ta dauka, a wani hukunci da ya yanke kan wata takardar kara da wasu jahohin Arewa uku da suka hada da Kaduna, Kogi da Zamfara suka gabatar.
Jihohin ukun dai sun gabatar da bukatar a ba su umarni na wucin gadi na hana gwamnatin tarayya ta hannun Babban Bankin Najeriya (CBN) ko kuma bankunan kasuwanci dakatar da amfani da wasu daga cikin kudaden Nigeria a ranar 10 ga Fabrairu, 2023.
Da yake gabatar da bukatar a ranar Laraba, lauyan wadanda suka shigar da kara, Mista A. I. Mustapha, SAN, ya bukaci kotun kolin ta amince da bukatar domin tabbatar da adalci da kuma jin dadin al’ummar Najeriya.
Ya bayyana cewa manufar gwamnati ta haifar da “mummunan yanayi wanda kusan ke haifar da rikici a cikin ƙasar”.