Ba za mu kara wa’adin Chanjin kuɗi daga 10 ga Fabrairu ba, Emefiele ya gargadi ‘yan Najeriya

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

 

Babban bankin Najeriya (CBN) ya ce ba ya tunanin kara tsawaita wa’adin karɓar tsoffin kudaden da aka sauya musu fasali ba.

 

 

‘Yan Najeriya ciki har da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC, sun bukaci babban bankin kasar da ya kara tsawaita wa’adin, sakamakon karancin kudin da aka yi wa kwaskwarima a cikin al’umma.

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Sai dai gwamnan babban bankin na CBN, Godwin Emefiele, ya ce bankin ba ya tunanin tsawaita wa’adin bayan wa’adin kwanaki 10 da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da shi kwanan nan.

 

 

Emefiele, wanda ya bayyana hakan a wani taron karawa juna sani da aka yi a Legas, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi hakuri ganin cewa nasarorin da aka samu a manufofin sun fi kalubalen yawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...