Ku magance matsalar ƙarancin kuɗi da yan ƙasar suke fuskanta – Atiku ya fadawa CBN

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

 

Ɗan takarar shugabancin Najeriya ƙarƙashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya yi kira ga Babban Bankin ƙasar CBN da ya magance wahalhalun da ‘yan ƙasar ke fuskanta na ƙarancin sabbin takardun kuɗi a faɗin ƙasar.

 

A wata sanarwa da ofishin yaƙin neman zaɓensa ya fitar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya gaggauta sake duba matakan da ya ɗauka, domin ya wadata al’umma da sabbin takardun kuɗin.

 

Yayin da yake yaba wa Babban Bankin kan sauraron koken talakawan ƙasar, tare da yin ƙarin wa’adin kwana 10 na amfani da tsoffin takardun kudin ƙasar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya sake duba matakan da ya ɗauka domin tabbatar da cewa an samu wadatattun sabbin takardun kuɗin a cikin al’umma.

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...