Ku magance matsalar ƙarancin kuɗi da yan ƙasar suke fuskanta – Atiku ya fadawa CBN

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

 

Ɗan takarar shugabancin Najeriya ƙarƙashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya yi kira ga Babban Bankin ƙasar CBN da ya magance wahalhalun da ‘yan ƙasar ke fuskanta na ƙarancin sabbin takardun kuɗi a faɗin ƙasar.

 

A wata sanarwa da ofishin yaƙin neman zaɓensa ya fitar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya gaggauta sake duba matakan da ya ɗauka, domin ya wadata al’umma da sabbin takardun kuɗin.

 

Yayin da yake yaba wa Babban Bankin kan sauraron koken talakawan ƙasar, tare da yin ƙarin wa’adin kwana 10 na amfani da tsoffin takardun kudin ƙasar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya sake duba matakan da ya ɗauka domin tabbatar da cewa an samu wadatattun sabbin takardun kuɗin a cikin al’umma.

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...