Kotu ta Aike da Shahararriyar ‘Yar TikTok Murja Kunya Zuwa Gidan Yari

Date:

Daga Nazifi Bala Dukawa

 

Babbar kotun shari’ar musulunci dake filin hokey ta aike da murja Ibrahim kunya zuwa gidan gyaran Hali.

 

Kadaura24 ta rawaito an gurfanar da ita a gaban kotun inda aka zargeta da laifukan bata suna, tayar da hankali da kalaman batsa da barazana.

 

Lauya mai gabatar da Kara lamido Abba soron dinki shi ne ya karanta mata kunshin tuhume-tuhumen da ake yi mata, Inda nan take ta musanta zargin.

 

Lauyan Murja Ibrahim Kunya Barr. Yasir Umar Musa ya nemi da a sanyata a hannun belli .

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Alkalin babbar kotun shari’ar musuluncin dake zaman ta a filin hocky Mai Sharia Abdullahi halluru abubakar ya yi umarni da kai Murja zuwa gidan yari, sannan yace a mai da ita gaban kotu ranar 16 ga wata domin bayyana matsayar kotu Kan Neman bellin.

 

Lauyan Murja kunya ya nemi da’a kaita hisbah kafin waccan rana domin dai yimata wa’azi da nasiha kan zargin da akai mata.

 

A bakon da ya gabata ne Kadaura24 ta rawaito cewa rundunar yan sandan jihar kano ta kama Murja Ibrahim Kunya wacce ta shahara wajen yin kalaman batsa da zage-zage a dandalin sada zumunta na TikTok.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...