Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kammala shirye-shiryen tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari da zai zo ziyarar aiki domin kaddamar da wasu ayyukan raya kasa guda takwas a jihar.
Kadaura24 ta rawaito Wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar ta ce gwamna Abdullahi Umar Ganduje zai karbi bakuncin shugaban kasar da shi da mukarrabansa.

Ya ce idan ya zo Kanon, Buhari zai kaddamar da gidan wuta na kano mai karfin megawatt 10, da Dala Inland Dry Port dake a Zawachiki, karamar hukumar Kumbotso.

Sauran aiyukan da zai bude sune hukumar adana bayanai ta jihar Kano da ke Audu Bako Secretariat, kamfanin Galaxy Backbone Limited Project da ke titin Ahmadu Bello Way.
Sauran sun hada da cibiyar kula da Masu cutar daji a asibitin kwararru na Muhammadu Buhari, Giginyu; Gadar Muhammadu Buhari dake NNPC, kan titin Maiduguri; cibiyar koyar da sana’o’i ta Aliko Dangote Ultra-Modern Skill Acquisition Centre, Zaria Road da Rukunin Gidajen Gwamnatin Tarayya dake Gandun Sarki, Darmanawa.