Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnatin jihar Kano ta janye gayyatar da ta aike wa shugaban kasa Muhammadu Buhari na neman ya zo domin kaddamar da wasu ayyuka a jihar.

Da yake karin haske akan lamarin, Ganduje yace gwamnatin jihar ta dauki matakin cikin gaggawa ne saboda wasu dalilai kaucewa sake.

Wani dalili kuma da ya tilastawa gwamnatin jihar janye gayyatar yana da alaka da wani gagarumin aiki da Buharin zai bude a Tiga wanda jami’an tsaro suka bada shawarar kar yaji garin Tigan domin bude gidan wutar da Ganduje ya samar.
” Gwamnatin jihar na jiran ji daga fadar shugaban kasar kan bukatar janye ziyarar Shugaba Buharin”. A cewar Ganduje