An maka wani mai gidan haya a kotu bisa yage kwanon rufin ƴan-haya

Date:

Daga Abdullahi Danbala Gwarzo

 

A yau Alhamis ne wata mai gidan haya mai suna Temitope Olayiwola mai shekaru 45 da ta cire rufin gidan ƴan haya, ta gurfana a gaban wata babbar kotun majistare ta Sabo-Yaba da ke Legas.

 

Olayiwola da ke Plot na 15 a rukunin gidaje na Oyadiran, Sabo-Yaba, Legas, ta musa laifuka biyu da ake tuhumar ta da su na rashin zaman lafiya da lalata da gangan.

 

Mai gabatar da kara, SP. Thomas Nurudeen, ya shaida wa kotun cewa Olayiwola ta aikata laifin ne a ranar 10 ga watan Disamba, 2022, a Plot 15 Oyadiran Estate, Sabo-Yaba, Legas.

Talla

Ya yi zargin cewa Olayiwola da gangan ta cire rufin kwanon na Edem Yves da Evans Anyanwu, wadanda ke haya a gidanta.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Nurudeen ya bayyana cewa Olayiwola ta dauki matakin lalata rufin gidajen ne bayan da ta yi yunkurin biyansu kudin haya.

 

A cewarsa, laifukan sun ci karo da tanadin sashe na 168 da 350 na dokokin laifuka na jihar Legas, na 2015.

 

Alkalin kotun, Mista Peter Nwaka, ya amince da bayar da belin Olayiwola a kan kudi N600,000 tare da mutane uku da za su tsaya mata.

 

Bayan haka, ya dage sauraron karar har zuwa ranar 13 ga Maris, domin ci gaba da Shari’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...