Daga Rahama Umar Kwaru
Hukumar gudanarwar Jami’ar Bayero ta Kano ta karyata rahoton da ke cewa jami’ar ta kara kudin makaranta.
A wata sanarwa da mataimakin magatakardar mai kula da harkokin jama’a Malam Lamara Garba ya raba wa manema labarai a Kano, ya ce labarin da aka yada bashi da tushe ballantana makama.

Sanarwar ta ce, “An jawo hankalin Hukumar Gudanarwar Jami’ar Bayero ta Kano game da wata wasika ta bogi da ake yadawa a shafukan sada zumunta inda ta sanar da karin kudaden makaranta.”

“Bisa la’akari da abubuwan da suka gabata, ya kamata dalibai da iyaye da sauran masu ruwa da tsaki su lura cewa har yanzu Jami’ar Bayero ba ta yanke shawara kan karin kudin makaranta ba, sabanin yadda wasu marasa kishin al’umma suke yada labaran karya a shafukan sada zumunta.
Sai dai sanarwar ta yi kira ga jama’a da su yi watsi da bayanan da ake yadawa su dauke su a matsayin labaran na bogi .