Wasu Mutane biyu sun rasu sakamakon fadawa masai a kano 

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Wasu ’yan uwa juna guda biyu, Abdullahi Rabi’u mai shekaru 17 da Musa Abdullahi, sun rasa rayukansu a wani bayan gida yayin da suka fada cikin shadda, a layin Abacha dake kasuwar sabon gari a karamar hukumar Fagge Kano.

 Rahotanni sun nuna cewa, lamarin ya faru ne yayin da mutanen biyu suka yanke shawarar share ban dakunan dake da ke karkashin kulawar su domin yin amfani da su cikin tsafta.
 Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Alhaji Saminu Abdullahi, ya bayyana cewa, Musa ya fita daga hayyacinsa ne a lokacin da ya fada cikin masan , hakan tasa dan uwansa Rabi’u ya shiga ramin domin ya taimaka masa.
Talla
 Ya kara da cewa, Musa da Rabi’u dukkansu ma’aikatane a gidan wankan l, sun mutu sakamakon zafi da rashin iskar oxygen kafin isowar ‘yan kwana-kwana.
 Saminu Yusif ya bayyana cewa, jami’an hukumar kashe gobara ta jihar sun yi nasarar ceto su a sume, inda suka kai su asibitin musamman na Murtala Muhammad domin kula da lafiyarsu, daga bisani kuma likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
 “Mun sami kiran gaggawa da misalin karfe 08:41 na dare. Daga wani Nasir Muhammed cewa mutane biyu sun fada cikin masai .
 Saminu ya kara da cewa, an mika gawarwakin wadanda abin ya shafa ga sufeto Abubakar Alhassan na sashin ‘yan sanda na Sabon Gari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...