Dan majalisar Wudil da Garko ya kaddamar da aikin wani titi da ya shekara 30 da lalacewa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

 

Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Wudil da Garko Hon. Engr. Muhd Ali Wudil ya kaddamar da aikin wata hanyar layin gidan alhazai zuwa shagari quarters dake karamar hukumar Wudil, wadda ta shekara talatin da lalacewa.

 

Kadaura24 ta rawaito yayin da yake kaddamar da aiki Dan majalisar ya ce zai gudanar da aikin ne domin saukaka al’ummar yankin duba da yawan al’ummar da suke amfani da titin a kodayaushe .

 

Talla

Engr. Muhd Ali Wudil yace baza a dauki lokacin Mai tsawo ba ana aikin, Inda ya bada tabbacin tunda aka fara akin titin mai tsahon kilomita guda baza a tsayaba sai an kammala shi domin amfani al’ummar yankin.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

” Mun San yadda wannan titi yake da matukar muhimmanci musamman wajen kai marasa lafiya asibiti, da kuma gudanar da harkokin ku na yau da kullum, hakan tasa na gudirci aniyar gyara titin don kuma ku daina Shan wahalar titin, Kuma na tabbata hakan zai inganta harkokin ku na yau da kullum harma da tattalin arzikin wanann yankin”. Inji Dan majalisar

 

Yace ya ga wannan aikin yanzu haka ma ana gudanar da aikin wasu hanyoyin wadanda suka hadar da titin cikin garin Wudil kofar yamma da Kuma titin indabo zuwa wudil dukkanin su yanzu haka ana aikin Kuma tunda aka fara babu wanda aka tsaya a cikin su.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...