Daga Nura Abubakar Cele
Dan takarar Dan majalisar tarayya na kananan hukumomin kura madobi da garun Mallam a jam’iyyar APC Hon. Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso, ya bayyana muhawarar yan takarar gwamnan kano da BBC Hausa suka shirya a matsayin wata hanya data Kara fito da kwarewa da nasarar Dr. Nasiru Yusuf Gawuna.
Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ganawarsa da jaridar kadaura24.

Yace Dr. Nasiru Gawuna wanda shi ne dan takarar gwamnan kano na jam’iyyar APC, ya kara nunawa duniya irin kwarewar da yake da ita wajen sanin matsalolin Kano, da kuma hanyoyin magance su da kuma yadda zai ciyar da jihar kano gaba idan Allah yasa ya lashe zaben.
- ” Dubi irin amsoshin da ya bayar game da tambayoyin da akai masa, ka da ji kasan kwarewar su ba iri daya bace da ta sauran yan takarar, Kuma hakan ya kara fito da kimar da aiyukan da gwamnatin jihar kano ta gudanar karkashin jagorancin Shugaban mu Dr. Abdullahi Umar Ganduje”. Inji Kwankwaso

” Wasu daga cikin yan takarar ma fa tambayar da akai musu ba amsarta suka rika bayarwa ba, shi kuwa dan takarar gwamnan jam’iyyar Yan gwari ficewa ma yayi daga dakin muhawarar Saboda bashi da abun da zai fadawa mutane kano, Kuma haka ya nuna ko da ya zama gwamna sai yafi fifita bukatun uban gidansa akan mutanen kano”. Musa Iliyasu Kwankwaso
Dan takarar dan majalisar na kura madobi da garun Mallam a jam’iyyar APC, yace babu shakka ficewar Abba Gida-gida daga wajen muhawarar ya tabbatarwa al’ummar jihar kano cewa bai shirya su zabe shi gwamnan su ba, saboda ya kasa fada musu yadda zai mulke su.
Yace al’ummar jihar kano yanzu ya ragewa ranar zabe su fito su zabi Dr. Nasiru Gawuna da Murtala Sule Garo, domin aiwatar da kyawawan manufofin su wadanda yake da yakin zasu kara daga darajar Kano a idanun duniya.