An Sami likitocin bogi 199 Cikin 280 da Ake Biya Albashi a Zamfara – Matawalle

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

 

Gwamna Bello Mohammed Matawalle na jiha zamfara ya ce gwamnatinsa ta gano likitocin bogi 199 da ake albashin gwamnatin jihar.

 

 

Ya ce gwamnatin jihar tana biyan albashin “likitoci 280 amma akwai likitoci 81 kawai na gaske a jihar .

 

 

Matawalle ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai a gidansa da ke garin Maradun, hedikwatar karamar hukumar Maradun ta jihar, inda ya kara da cewa lamarin ya sa gwamnatin jihar ta fuskantar mawuyacin halin wajen biyan albashin su na wata-wata.

Talla

 

Ya ce ya gana da jami’an kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar da sauran masu ruwa da tsaki kan yadda za a binciko wadancan likitocin bogi guda 199 da suka dauki tsawon lokaci suna karbar albashi ba bisa ka’ida ba da nufin gyara matsalar.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

“Masu ruwa da tsakin sun tabbatar min da cewa dalilin da ya sa aka jinkirta biyan albashin ma’aikatan kiwon lafiya shi ne yadda suke son tabbatar da cewa al’amura sun tafi daidai kuma nan ba da dadewa ba za mu magance dukkan matsalolin a bangaren lafiya.

 

 

“Na biya albashin watan Nuwamba da Disamba ga dukkan ma’aikatan lafiya amma abin takaici mun gano rashin jituwa kan yadda ake biyan albashin,” in ji Matawalle.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...