INEC ta tsawaita lokacin rufe karɓar katin zaɓe

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Hukumar zaɓe a Najeriya (INEC) ta tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓe da take raba wa a faɗin ƙasar.

 

INEC ta tsawaita wa’adin da kwanaki 8.

Talla

Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na INEC, Festus Okoye ya ce an ɗauki matakin ne don bai wa masu kada kuri’a isasshen lokaci na karɓar katin kafin fara jefa ƙuri’a a babban zaɓe na 2023.

 

“Saboda wannan dalilin, an tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓen da kwana takwas,” in ji shi.

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

“A maimakon 22nd ga watan Janairu, za a ci gaba da karɓa har zuwa Lahadi, 29 ga watan na Janairu.”

 

INEC ta ce lokacin karɓar katin shi ne 9:00 na safe zuwa 3:00 na yamma a kullum da ga Asabar zuwa Lahadi.

 

Kazalika, tsawaitawar ta shafi dukkan cibiyoyin karɓar katin a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu .

 

A ranar 25 ga watan Fabarairu ne za a fara kaɗa ƙuri’a, inda ake sa ran yan kasa miliyan 93.4 million da su ka yi rijistar zaɓe za su zaɓi shugaban ƙasa da ‘yan majalisar tarayya.

 

Sai kuma gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da za a zaɓa a watan Maris

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...