Ganduje Ya Nada Yusuf Datti A Matsayin Babban Sakataren Ma’aikatar Kananan Hukumomi

Date:

Daga Halima Musa Sabaru
 Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya amince da tura Yusuf Datti Husaini ma’aikatar kananan hukumomi ta jiha a matsayin sabon babban sakatare na ma’aikatar.
Gabanin tura shi ma’aikatar, Sabon baban sakataren tsohon darakta albashi ne na ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu ta jiha .
Talla
Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran gwamna Malam Abba Anwar ya sanyawa hannu kuma aka aikowa kadaura24.
 Bayan rantsar da shi yau Alhamis a gidan gwamnati, gwamna Ganduje ya umarce shi da ya kasance a shirye a kodayaushe ya amince da ci gaban fasaha a aikin gwamnati tare da yarda da mafi kyawun aiki na duniya.
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
  •  “ bayanai sun nuna kana da kwarewa kuma ka cancanci sabon matsayin da aka baka, muna sa ran ka ci gaba da yin kyakkyawan wannan tarihi da kake da shi a aikin gwamnati,” inji shi.
 Gwamna Ganduje ya umurci sabon babban sakataren ya yi aiki tukuru tare da yin aiki tare da dukkan ma’aikatansa a ma’aikatar don ganin an sami nasarar da ake fata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...