Akwai bukatar Kwararrun ma’aikatan gwamnati musamman idan gwamnatin ta zo ƙarshe – Ganduje

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya jaddada bukatar samun ma’aikata masu kwazo da himma musamman a karshen kowace gwamnati.

 

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya jagoranci rantsar da wani sabon babban sakatare Alhaji Yusuf Datti Husain a gidan gwamnati.

 

Talla

Ya bayyana cewa akwai bukatar samun irin wadannan jajirtattun ma’aikata masu gaskiya don ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati don samun nasarar mika mulki daga wata gwamnati zuwa wata .

 

Gwamnan ya bayyana cewa sabon babban sakataren kafin nada shi sai da aka duba dimbin gogewarsa da himmarsa yayin da ya yi aiki a ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu ta jihar kano.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

 

Gwamna Ganduje ya kuma umarci sabon sakataren da ya ci gaba da gudanar da aikinsa bisa gaskiya da jajircewa don cimma manufofin da aka sa gaba.

 

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan gwamnati M. A Lawal ne ya rantsar da sabon sakataren na Alhaji Yusuf Datti Husain daga karamar hukumar Dawakin Kudu.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...