Akwai bukatar Kwararrun ma’aikatan gwamnati musamman idan gwamnatin ta zo ƙarshe – Ganduje

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya jaddada bukatar samun ma’aikata masu kwazo da himma musamman a karshen kowace gwamnati.

 

Gwamna Ganduje ya bayyana hakan ne a lokacin da ya jagoranci rantsar da wani sabon babban sakatare Alhaji Yusuf Datti Husain a gidan gwamnati.

 

Talla

Ya bayyana cewa akwai bukatar samun irin wadannan jajirtattun ma’aikata masu gaskiya don ci gaba da gudanar da ayyukan gwamnati don samun nasarar mika mulki daga wata gwamnati zuwa wata .

 

Gwamnan ya bayyana cewa sabon babban sakataren kafin nada shi sai da aka duba dimbin gogewarsa da himmarsa yayin da ya yi aiki a ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu ta jihar kano.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

 

Gwamna Ganduje ya kuma umarci sabon sakataren da ya ci gaba da gudanar da aikinsa bisa gaskiya da jajircewa don cimma manufofin da aka sa gaba.

 

Kwamishinan shari’a kuma babban lauyan gwamnati M. A Lawal ne ya rantsar da sabon sakataren na Alhaji Yusuf Datti Husain daga karamar hukumar Dawakin Kudu.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...