Cikin Watanni 3 Likitoci sama da 170 Sun Bar Aiki a jihar Kwara – Gwamnan jihar

Date:

Daga Zara Jamilu Isa

 

Gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq ya koka da yadda kwararrun likitoci sama da 170a jihar suka bar aikin gwamnati a cikin watanni ukun da suka wuce .

 

Da yake jawabi a wajen kaddamar da wata cibiyar kular kula da lafiya ta zamani da aka gina akan kudi Naira miliyan 350 da ke babban asibitin garin Offa a karamar hukumar Offa a jihar Kwara, wanda wata kungiyar ‘yan asalin yankin Offa Metropolitan Club (OMC) suka gina a ranar Asabar, gwamnan ya ce gwamnatin jihar ba zai iya kula da sha’anin kiwon lafiya ita kadai ba.

 

Talla

“Mu a Kwara, muna samun kalubalen yadda likitocn mun suke komawa asibitocin gwamnatin tarayya wasu kuma suna komawa Legas da Abuja, yayin da su kuma na Legas sume komawa kasashen Ingila, Amurka, da sauran kasashen turai. Wannan shi ne ɗayan daga cikin manyan ƙalubalen da muke fuskanta”. inji Gwamnan

 

Dan takarar sanata da na majalisar wakilai sun ajiye takarar sun fice daga jam’iyyar NNPP a Zamfara

Gwamnan wanda ya nuna jin dadinsa kan wannan aiki, ya ce gwamnatin jihar za ta tallafa wa shirin domin amfanin jama’a.

“A cikin watanni uku da suka gabata, mun yi asarar likitoci 170 a ma’aikatan jihar. Wannan yana daya daga cikin kalubalen da kuke da shi; samun kwararrun likitoci a biya su daidai. Adadin da muka rasa na likitoci da ungozoma yana Kara karuwa kullum, Yawancin wadancan likitocin kawai kudi ne a gabansu ba batun kishin kasa a gare su, hakan tasa sai barin jihohi da yawa suna rasa likitoci, ” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...