Rashin Albashi yasa Ma’aikatan Kogi sun koma bara

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Ma’aikatan da ke karkashin karamar hukumar Bassa a jihar Kogi sun fara kukan neman agaji saboda gazawar gwamnatin jihar wajen biyan su albashin watan Nuwamba.

 

DAILY POST a cikin wannan rahoto na musamman, ta yi duba ne kan yadda rikicin karamar hukumar Bassa ya jefa ’yan fansho da ma’aikata a kananan hukumomi cikin mawuyacin hali.

Talla

Karamar hukumar Bassa dai ta fada cikin rikici tun a shekarar 2016, inda aka kashe mutane da dama, aka lalata gidaje da kuma raba ‘yan asalin yankin da muhallansu, Rikicin dai ya faru ne tsakanin Bassa Komu da Egbira Mozum. DAILY POST ta tattaro cewa kabilun biyu suna takun-saka a tsakaninsu kan takaddama akan kamun kifi.

Gwamnati dai ta kafa kwamitin bincike don duba rikicin amma ba a yi komai ba. Wannan ci gaban ya kara dagula matsalar mutanen da ke aiki a karamar hukumar Bassa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...