Kotu ta bada umarnin kwace kudi sama da Dala 899 daga tsohon akanta janar na Nigeria

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Wata babbar kotun a Najeraya ta bayar da umarnin kwace dala 899, 900 da naira miliyan 304, 490, 160. 95 da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta kasar EFCC ta karbo daga hannun tsohon Akanta Janar din Najeirya Ahmed Idris.

 

Mai shari’a M. A Haasan ne ya bayar da umarnin a zaman kotun a ranar 13 ga Disambar da muke ciki, yayin da yake yanke hukunci kan ƙarar da hukumar EFCC a Najeriya ta shigar gabanta.

 

Haka kuma kotun ta umarci da a karbe kadarori 15 mallakinsa da ke Kano da Abuja.

Talla

Kadarorin da aka bayar da umarnin a kwace sun haɗa da babban kantin sayar da kaya na Al-Iklas, da wasu shaguna a Ladanai, da gidan gidan alfarma na unguwar Daneji dukkan su da ke Kano.

 

Haka sai gidansa da ke Karsana a Abuja, da wani plotin, dake rukunin gidaje na Blue Fauntain shima a baban birnin Najeriyar Abuja.

 

Hukumar EFCC ta gurfanar da Ahmed Idris da ƙarin wasu mutane, gaban kotun ne kan zargin aikata wasu laifuka 14 da ke da alaƙa da sata da halarat kuɗin haram da kiyasin su ya kai naira bilyan109.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...