Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Masu ababen hawa na ci gaba da kokawa game da karancin man fetur da kuma tsadarsa a jihar Kano.
Wannan na zuwa ne bayan da jami’an tsaron farin kaya a jihar Kano suka yi wata ganawa da dillalan man fetur din game da karancinsa.
Gidajen mai da dama na sayar da shi kan fiye Naira 300 kowace lita, kuma kuma a rufe babu man.
Gidajen man da ake sayar da shi a farashin gwamnati kuwa sai mutum yaci kwakwa kafin ya samu saboda dan karan layi.

Game da wannan matsalar mai ne, hukumar tsaro ta DSS ta yi wata ganawa da dillalan man fetur a Kano cikin wannan mako.
Bayanai na cewa wasu dillalan man na boye shi ba tare da wani dalili ba.
Sai dai Shugaban kungiyar dillalan man IPMAN, reshen arewacin Najeriya, Bashir Dan Mallam, ya ce sun tattauna sosai da jami’an tsaron.
A farkon makon nan ne, majalisar dokokin Najeriya ta umarci kamfanin mai na NNPC da hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur da kuma dillalan man fetur da su yi duk mai yiwuwa cikin mako guda su kawo karshen matsalar man fetur, tare da tabbatar da sayar da man a farashi man rangwame.