Daga Rahama Umar Kwaru
Kotu ta ce, ta samu Abduljabbar Kabara da laifin yiwa ma’aiki (s a.w) kage da cin mutumcin ma aiki da cewar yayi fyade, an same shi da laifi karkashin sashe na 382 (B)
Lauyan da ke kare shi Barrister Aminu Abubakar yace yayi masa sassauci saboda kuskuren fahimta ce tasa Malam Abduljabbar ya aikata wannan laifi.

Amma nan take malamin ya miƙe ya ce shi dai ba da yawunsa ba, Lauyana yake magana”.
Freedom Radio ta rawaito Malamin ya ce, baya neman sassauci, kuma yana neman a gaggauta yi masa hukunci domin zai yi mutuwa ta girma.
Ku ci gaba da bibiya, zamu ci gaba da kawo muku yadda take kasancewa.