Gine-gine kimanin 5,000 aka rushe wadanda aka yi a ƙarƙashin manyan layukan lantarki a Najeriya

Date:

 

Shugaban hukumar kula da harkokin wutar lantarki a Najeriya ta Nigerian Electricity Management Service Agency (NEMSA) ya ce sun rusa gine-gine kusan 5,000 da ke ƙarƙashin manyan wayoyin lantarki a faɗin ƙasar.

 

Aliyu Tahir wanda shi ne kuma babban jami’in lantarki na ƙasa, ya faɗa a yau Juma’a cewa tun 2017 aka ɗauki mataki tare da ba da umarnin rushe gine-ginen da ke ƙarƙashin wayoyin, kamar yadda kamfanin labarai na NAN ya ruwaito.

 

NEMSA ta ce akwai buƙatar gaggauta katse yankunan daga layin lantarki da kuma rushe su daga baya.

Talla

 

“A ɓangarenmu, mun bai wa kamfanonin rarraba lantarki umarnin sauke duk wani gini da aka yi a ƙarƙashin babban layin lantarki daga kan layin wutar, har ma da waɗanda suka tare hanya,” a cewarsa.

 

Tahir ya ƙara da cewa rushe gine-ginen na buƙatar himma daga waɗanda abin ya shafa, “kamar gwamnatin tarayya da ta jihohi”.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...