Daga Aisha Aliyu Umar
Hukumar gudanarwar gidan talabijin ta Abubakar Rimi ARTV sun karrama wasu ma’aikatan ta bisa kwazon da suka nuna a yayin aikinsu a wannan shekara ta 2023 da ke karewa.
Dama dai duk shekara hukumar gidan talabijin din takan zabo wasu daga cikin ma’aikatan ta daga sassa daban-daban na gidan don karrama su bisa kokarin da sukai a wanna shekara.
Da yake jawabi a wajen taron Kwamishinan yada labarai na jihar kano Com. Muhd Garba ya ce irin wadannan kuautata wa da ake yiwa ma’aikatan zata Kara musu kwarin gwiwa ta Kuma zaburar da sauran ma’aikata.

” Irin wannan karawa ma’aikata karsashi, don haka ina kira ga sauran ma’aikatu da suke karkashin Ma’aikatar yada labarai dasu yi koyi da irin wannan salon na ARTV domin inganta aiyukan su”. Inji Muhd Garba
Itama a nata jawabin shugabar gidan talabijin din Hajiya Sa’a Ibrahim ta ce ta kirkiro bada lambobin yabon ne shekaru 4 da suka gabata domin karawa ma’aikatan ta kwarin gwiwa.
Tace an bi hanyoyin da suka dace wajen zabo wadanda aka baiwa lambar yabon daga sassa daban-daban na gidan talabijin din, ta Kuma yabawa gwamnatin jihar kano bisa gudanar da take baiwa tashar.
Daga cikin wadanda aka karrama akwai wakilin Gidan Tv a ofishin gwamnan jihar kano Wato Abdullahi Hassan wanda ya zamo Gwarzon shekara cikin masu aike da rahoto da dai sauransu.