Waɗanda suke gayyata ta muhawara kudi kawai suke neman da ni don sun ga ina da jama’a —Tinubu

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya

 Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Tinubu, ya ce masu gayyatarsa ​​zuwa muhawara suna kokarin amfani da shi ne kawai don samun kudi domin shi mutum mai tarin jama’a.
 Tsohon gwamnan jihar Legas ya bayyana haka ne a gidan Chatham da ke birnin Landan ranar Litinin, sa’o’i 24 bayan da ya yi watsi da wata muhawara da wasu ‘yan takara uku suka halarta a zaben shugaban kasa na 2023.
Talla
 Da yake amsa tambayoyi daga masu sauraro a kan dalilin da ya sa ya yi watsi da muhawarar, Tinubu ya ce, “Ina ganin kaina a matsayin mutum mai mutane, Kuna so ku yi amfani da ni don samun kuɗi kuma na ce ki.”
 Dangane da cece-kucen da ya shafi shekarunsa, makaranta da lokacinsa a kamfanoni masu zaman kansu, ya ce, “A tarihin gidanmu anhaife ni a ranar 29 ga Maris, 1952, Sannan, lokacin ban ma a raina cewar zan zama shugaban Tarayyar Najeriya ba, ballantana ma nace zan shiga siyasa.
 “Ina da kyakkyawan tarihi har a makarantar jami’ar da suke tambaya a kai suje su tambaya, bata lokacin su kawai zasu yi domin komai yana nan a rubuce a watan maris din 1952 aka haife ni.
 “Daya daga cikinsu ma an zarge shi da cewa ba dan Najeriya ba ne, bana irin wannan maganar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related