Rundunar sojin Sama ta kashe ƙasurguman ƴan fashin daji da ke addabar jihar Zamfara

Date:

Daga Daga Maryam Ibrahim zawaciki

 

 

Rundunar sojojin sama ta Najeriya tace jami’anta sun samu nasarar hallaka wasu ƙasurguman ƴan fashin daji waɗanda ke addabar ƙauyukan jihar Zamfara.

 

Rahoton Jaridar PRNigeria ya nuna cewa an samu nasarar kashe ƴan fashin ne a wasu hare-hare da jiragen sojojin Najeriya suka kai a wasu ƙauyukan jihar Kaduna.

 

Waɗanda aka kashen a cewar rahoton sun haɗa da Jibrin Gurgu, da Isah Jauro da kuma wani da ake kira Tambuwal.

 

Talla

Sauran sun haɗa da Noti, da Bala, da Yunusa da kuma Burti.

 

Bayanin da jaridar ta samo ya ce an kai farmakin ne a wasu sabbin sansanonin ƴan fashin a yankin ƙaramar hukumar Giwa da ke jihar Kaduna.

 

Haka nan an kai wasu hare-haren a yankunan ƙananan hukumomin Igabi da Birnin Gwari.

 

Wata majiyar tsaro ta ce an ga dacewar kai harin ne bayan rahotannin da ke cewa an samu ƙaruwar ayyukan ƴan bindiga a yankin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...