EFCC ta fara farautar dan takarar Sanatan Kano ta tsakiya A A Zaura

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon ƙasa ta bayyana neman ɗan takarar Sanatan Kano ta tsakiya a ƙarƙashin jam’iyyar APC mai mulki, AbdulKareem AbdulSalam Zaura wanda aka fi sani da A.A Zaura.

 

Lauyan hukumar EFCC, Ahmad Rogha ne ya bayyana haka ga manema labarai ranar Litinin bayan da aka dawo da batun shari’ar dala miliyan 1.3 da ake yi wa A.A Zaura a babbar kotun tarayya da ke Kano.

 

Talla

Duk da cewa shari’ar da aka shirya yi wa ɗan siyasar ba ta samu ba, saboda rashin halartar alkalin da ke sauraron shari’ar, wanda aka ce yana halartar wani taron ƙasa a wajen birnin na Kano.

 

Haka kuma lauyan na EFCC ya bayyana cewa ya kamata A.A Zaura ya kai kansa ga hukumar.

 

“Muna neman Zaura kuma za mu kama shi da zarar mun same shi”.

 

”A ƙa’ida, ya kamata a ce yana hannunmu domin kuwa kotu ta tabbatar da haka, amma ina tabbatar da cewa za a kama shi tare da gurfanar da shi a gaban kotu a zamanta na gaba ranar 30 ga Janairun 2023”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...