Gobara ta kone wata makarantar firamare a kano

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

 

Wata gobara da ta tashi da yammacin ranar lahadi har ta kone wata makarantar tsangaya firamare ta kwana da ke kauyen Kiyawa da ke karamar hukumar Bagwai a jihar Kano.

 

 

Rahotanni sun nuna cewa, gobarar ta lalata gaba daya ajujuwa 14 da ofisoshi 12 da bandakuna 21, dake cikin harabar makarantar.

 

 

Da yake bayyana yadda lamarin ya faru, jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, PFS Saminu Yusif Abdullahi ya bayyana cewa, hukumar kashe gobara ta Bichi ta samu kiran gaggawa daga Alhaji Ghadafi Sani Bagwai.

 

Talla

 

Ya kara da cewa, da isar da tawagar jami’an hukumar wurin sun gano cewa wani gini mai tsawon kafa 400 zuwa 400 wanda ake amfani da shi a matsayin makarantar kwana ta Tsangaya Model, ya kone baki daya

Laifin Iyaye da shugabanni ne yasa matasa suke shiga bangar siyasa – Aminu Danjimmai

 

Saminu Yusif ya jaddada cewa, gobarar ta tashi ne daga babban ginin da ke kan hanyar sadarwa, bayan da na’urar hasken rana ta lalace, ta kuma bazu zuwa wasu sassan makarantar Tsangaya.

Ana amfani da sunan Hakimin T/Wada ana kwace mana gonakin mu – al’ummar wani gari suka koka

 

Jami’in hulda da jama’ar ya yi nuni da cewa, ba a samu asarar rai ba a lokacin da lamarin ya faru, domin an yi nasarar kwashe dukkan daliban tsangayar.

 

 

Ya jaddada jajircewar hukumar wajen kare rayuka da dukiyoyin mazauna Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...