Yan sanda sun gano gidan sayar da jarirai a Nasarawa

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Rundunar ‘yan sanda Nasarawa da ke Najeriya ta ce ta gano gidan da ake zargin sayar da jarirai a karamar hukumar Karu na jihar.

 

Rundunar ta ce ta ceto mata shida da kuma jariri ɗan wata shida a gidan.

 

A sanarwar da suka fitar, jami’in hulda da jama’a na yansanda yankin, DSP Ramhan Nansel ya ce da misalin 2 na rana suka kai samame Karu bayan samun wasu bayanan sirri.

Talla

Ya ce ana basaja da gidan ne a matsayin gidan kula da marayu. Sai dai bincike ya gano cewa ana garkuwa da kananan yara ana yi musu ciki sannan a sayar da jariran da suka haifa.

 

An dai cafke wasu mutum uku da ake zargin ke aikata wannan muggun aika-aika.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...