Sha’aban Sharada ya yi alkawarin sanya dokar ta baci a bangaren Ilimi, Idan ya zama gwamnan kano 

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

Dan takarar gwamnan jihar Kano, a ƙarƙashin jam’iyyar ADP Sha’aban Ibrahim Sharaɗa, ya bada tabbacin sanya dokar ta baci a bangaren ilimi, a kokarin sa na ceto fannin jihar idan ya zama gwamnan jihar kano.

Sha’aban Sharaɗa ya bayyana hakan ne cikin wani jawabi da ya gabatar a yayin wani taron jin ƙudirin ƴan takar gwamna jihar Kano, a kakar zaɓe mai zuwa taron da Gidauniyar Dakta Aminu Magashi haɗin gwiwa da ƙungiyoyin farare hula na jihar su ka shirya.
Taron ya maida hankali kan batun yadda masu neman takarar gwamnan Kano za su inganta ɓangaren kiwon Lafiya da ilimi da , tsaro da kuma bunƙasa masana’antu da, samar idan su ka samu nasara.
Talla
Kazalika ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa za ta yi dukkanin mai yiwuwa wajen yin duba na tsanaki kan dokokin ilimi matuƙar ya samu nasara.
Haka kuma ɗan takarar gwamnan ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci sallamar malamai ba sai dai za a duba inda ya dace a sanya su.
A karshe Sha’aban Ibrahim Sharaɗa ya kuma bayyana cewa yana da tanadi na musamman kan ilimi a jihar Kano da kuma samar da kayayyakin yanayin koyo da koyarwa har ma da inganta manyan makarantun gaba da Sakandire.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...