Inganta Ilimi: Sarkin Kano ya hori daliban makarantu su rika tallafawa makarantunsu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nuna gamsuwarsa bisa gudumawar da tsofafin daliban Makarantar Firamaren ta Shahuchi suke bayarwa a fannin ilimi a makarantar.

 

Mai Martaba Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci makarantar domin duba wasu aiyuka da kungiyar tsofaffin dalibai sukayi na gyara wasu ajujuwa.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce mutukar tsofaffin dalibai za su rika taimakawa makarantun su hakan zai taimakawa gwamnati wajen ciyar da ilimi gaba a jihar nan dama kasa baki daya.

Talla

Cikin sanarwar da sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24,yace Alhaji Aminu Ado Bayero ya yabawa General Ibrahim Sani Mai ritaya sabo da gudumawar da yake bawa makarantar firamaren ta shahuchi.

Tattakin APC ya tabbatar Tinubu zai Sami kuri’a Miliyan 2 a Kano – Musa Iliyasu Kwankwaso

A nasa jawabin General Ibrahim Sani ya ce mutukar ya zama gwamnan jihar Kano a zabe shekarar 2023 zai bawa harkokin ilimi fifiko.

 

Shikuwa da yake nasa jawabin shugaban Makarantar Alhaji Umar Danbaba ya ce makarantar tana kira da gwamnatin data samar musu da jami’an tsaro da yawan malamai da dai sauran kayan aiki na zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...