Sikila: Kamata ya yi iyaye su rika tura ‘ya’yansu gwajin jini da zarar saurayi ya fara zuwa wajen ‘yar su- Yakubu Sa’id

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Kungiyar dake tallafawa masu fama da larurar cutar amosanin jini da wayar da kan al’umma muhimmancin yin gwaji kafin aure ta jihar kano, ta sha alwashin ci gaba da wayar da kan al’umma domin yin gwaji kafin a fadin jihar kano.

 

Shugaban kungiyar Alh muharazu Adamu Ibrahim Gizina ,Wanda mataimakinsa yakubu saidu ya wakilta ne ya bayyana haka a lokacin da kungiyar ta kai ziyarar wayar da kan matasa muhimmancin yin gwaji kafin aure, a makarantar sakandiren yan mata ta Bichi dake karamar hukumar Bichi .

 

 

Yakubu yace kasancwar cutar amosanin jini tana wahalar da kananan yara musamman a wannan lokaci na hunturu dake shigowa, shi yasa kungiyar ta kara kaimi da himma domin fadakar da al’umma musamman iyaye mahimmancin gwajin cututtuka da suka shafi yin ma’urata.

Talla

 

Yace gwajin cututtuka kafin a yi mu’amullar auratayya yana da mutukar mahimmanci musamman a wannan lokaci da cututtuka suka yi yawa ,Wanda akwai bukatar kulawa a kodayaushe domin kaucewa kamuwa daga cututtuka masu tarin yawa, wandanda a bayan ba’a san su ba.

 

A jawabinta shugabar makarantar sakandiren yan mata ta karamar hukumar Bichi, Hajiya Fatima Abubakar ta nuna farin cikinta bisa wananan ziyara da kungiyar ta kai makarantar sakandiren, domin wayar da kan al’umma da iyaye da ma yanmata amfanin yin gwaji kafin a yi aure.

 

Ta yi kira ga iyaye da masu hannu da shuni da uwa uba Gwamnatin wajen tallafawa yunkurin kungiyar na bata gudunmawar da ta kamata domin cimma nasarar da ta sanya a gaba.

 

Haka zalika, ta shawarci dalibai musamman yan mata da su kasance masu kulawa da kawunansu da tabbatar da nauin jininsu da kuma sana’ar da masu neman aurensu kan su je su yi gwaji kafin a yi nisa a cikin soyayyar juna, wadda ka iya kaiwa ga Aure.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...

Tinubu ka fadawa yan Nigeria Inda ka tsaya har kwana 5 bayan taron BRICS – ADC

    Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC ta soki Shugaban...

Da dumi-dumi: Yadda akai Jami’an tsaro suka kama ni -Danbello

Rahotannin sun tabbatar da cewa jami'an tsaro a Nigeria...