Sikila: Kamata ya yi iyaye su rika tura ‘ya’yansu gwajin jini da zarar saurayi ya fara zuwa wajen ‘yar su- Yakubu Sa’id

Date:

Daga Ibrahim Sani Gama

 

Kungiyar dake tallafawa masu fama da larurar cutar amosanin jini da wayar da kan al’umma muhimmancin yin gwaji kafin aure ta jihar kano, ta sha alwashin ci gaba da wayar da kan al’umma domin yin gwaji kafin a fadin jihar kano.

 

Shugaban kungiyar Alh muharazu Adamu Ibrahim Gizina ,Wanda mataimakinsa yakubu saidu ya wakilta ne ya bayyana haka a lokacin da kungiyar ta kai ziyarar wayar da kan matasa muhimmancin yin gwaji kafin aure, a makarantar sakandiren yan mata ta Bichi dake karamar hukumar Bichi .

 

 

Yakubu yace kasancwar cutar amosanin jini tana wahalar da kananan yara musamman a wannan lokaci na hunturu dake shigowa, shi yasa kungiyar ta kara kaimi da himma domin fadakar da al’umma musamman iyaye mahimmancin gwajin cututtuka da suka shafi yin ma’urata.

Talla

 

Yace gwajin cututtuka kafin a yi mu’amullar auratayya yana da mutukar mahimmanci musamman a wannan lokaci da cututtuka suka yi yawa ,Wanda akwai bukatar kulawa a kodayaushe domin kaucewa kamuwa daga cututtuka masu tarin yawa, wandanda a bayan ba’a san su ba.

 

A jawabinta shugabar makarantar sakandiren yan mata ta karamar hukumar Bichi, Hajiya Fatima Abubakar ta nuna farin cikinta bisa wananan ziyara da kungiyar ta kai makarantar sakandiren, domin wayar da kan al’umma da iyaye da ma yanmata amfanin yin gwaji kafin a yi aure.

 

Ta yi kira ga iyaye da masu hannu da shuni da uwa uba Gwamnatin wajen tallafawa yunkurin kungiyar na bata gudunmawar da ta kamata domin cimma nasarar da ta sanya a gaba.

 

Haka zalika, ta shawarci dalibai musamman yan mata da su kasance masu kulawa da kawunansu da tabbatar da nauin jininsu da kuma sana’ar da masu neman aurensu kan su je su yi gwaji kafin a yi nisa a cikin soyayyar juna, wadda ka iya kaiwa ga Aure.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...