Wike ya nemi afuwar Oshiomhole, ya kuma yi nadamar yin aikin sake zabar Obaseki

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamna Nyesom Wike na jihar Rivers a ranar Larabar da ta gabata ya nemi afuwar tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole, inda ya ce ya yi nadamar yin aiki domin sake zabar gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo a watan Satumban 2020.

 

Wike ya baiwa Oshiomhole hakuri ne a wajen kaddamar da jirgin Rumuepirikom Flyover a karamar hukumar Obio-Akpor ta jihar wanda Oshiomhole ya kaddamar.

 

Talla

 “Yanzu mun zama abokai, mu manta duk abun da ya faru a baya,” Wike ya shaida wa Oshiomhole cikin murmushi.

 

A baya-bayan nan dai, Obaseki da Wike sun sami sabani hakan tasa suke yi takun-saka Saboda rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP a daidai lokacin da Obasake ke goyon bayan Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, yayin da Wike ya ci gaba da neman Iyorchia Ayu da ya yi murabus a matsayin wani sharadi na goyon bayan takarar Atiku a zaben 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...