Sarkin Kano ya yabawa Kasar Egypt bisa samar da kamfanin shinkafa a kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya bayyana gamsuwar sa akan aikin da kasar Egypt zasu yi na samar da katafaran kamfani shinkafa wanda jihar Kano ce zata fi amfana da aikin a kasar nan.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero CFR ya bayyana haka ne lokacin da yake karbar bakuncin shugabanin Gwamnatin Kasar Egypt dangane da aikin samar da wani kamfanin samar da shinkafa da zasu kafa a nan jihar Kano.

 

Mai Martaba Sarkin yace dangantakar dake tsakanin kasar masar da Nigeria musamman jihar Kano dangantaka ce dake kara habaka tattalin arzkin Kano da kasa baki daya.

Talla

Cikin sanarwar da babban Sakataren yada labaran Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa ya ce, masarautar kano za ta bayar da gudunmawar data dace wajen ganin an samar da cigaban tattalin arzkin Kano da Nigeria baki daya.

 

Mai Martaba Sarkin ya kuma yabawa kasar ta masar bisa gudummawar da suke bayarwa wajen ilimantar da al’ummar a kasar nan.

 

A nasa jawabi Shugaban kamafanin Egta Alhaji Bashir Yusif Ibrahim yace, jihar Kano zata ci gajiyar samar da kamfanin shinkafa mafi girma a kasar nan wanda kasar masar zata samar a jihar kano.

 

Haka zalika a wani cigaban kuma Mai Martaba Sarkin na Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya karbi bakuncin shugabanin hukumar zakka da Hubsi ta jiahr Kano karkashin jagorancin shugaban majalisar limaman juma’a Sheikh Muhammad Nasir limamin masallacin Sheikh Ahmadu Tijjani dake Kofar Mata a Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...