Ba zan bari laifin wani ya shafe ni ba – Shugaban EFCC

Date:

Daga Aliyu Nasir Zangon Aya

 

Shugaban hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati EFCC AbdulRasheed Bawa ya ce ya daukaka kara dangane da hukuncin da wata kotun birnin tarayya ta yanke masa ranar Talata a Abuja.

 

Kotun yanke hukuncin tura shi gidan yari sakamakon kama shi da laifin raina umarnin kotu.

 

Tun da farko dai kotun ta umarci shugaban da ya mayar da wasu kudi da suka kai naira miliyan 40 da wata motar alfama da hukumar ta karba daga wani mutum da ta zarga da laifin rashawa.

 

Shugaban EFCCn ya ce shi a karan kansa bai yi watsi da umarnin kotun ba a matsayinsa na shugaban hukumar, ballantana ya fuskanci fushin kotu, saboda a saninsa kotun ta bayar da umarnin ne tun a ranar 21 ga watan Nuwamban 2018.

Talla

Wato shekara uku kenan kafin ya zama shugaban hukumar ta EFCC, dan haka ba shi aka bai wa umarnin ba kuma a cewarsa babu yadda za a yi laifin wani ya shafe,

 

Ya kara da cewa ”Mun riga mun daukaka kara game da wannan hukunci, dan haka za mu jira domin ganin yadda shari’ar za ta kasance”

 

Amma ya ce duk da haka ya bayar da umarni a mayar da wannan motar alfarma ga mai ita tun a ranar 27 ga watan Yunin wannan shekarar, tare da bayar da umarnin bin hanyar da ta dace wajen mayar da kudin naira miliyan 40 ga mai su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dr. Kabiru Getso Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Buhari

Daga Rahama Umar Gwaru   Tsohon kwamishinan ma'aikatun lafiya da muhalli...

Gwamnatin tarayya ta ayyana Ranar hutu saboda rasuwar Buhari

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana Talata, 15 ga watan...

Injiniya Iliyasu Usman Salihu ya zama Jakadan zaman Lafiya na Africa

    Injiniya Ilyasu Uasman Salihu, Manajan Darakta na Sadex Engineering...

Halin da ake ciki game da shirye-shiryen jana’izar Buhari

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda, ya bayayna cewa sai...