Muna da kyakyawar alakar sama da shekaru 100 tsakanin mu da Masarautar Kano – Sarkin Jama’are

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

 

Mai Martaba Sarkin Jama’are dake jihar Bauchi Alhaji Nuhu Ahmad Wabi ya jaddada alakar dake akawai tsakanin Masarautar Jam’are da ta Kano tare da cewa alakace mai dunbun tarihi.

 

Sabon Sarkin ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero CFR a fadarsa a safiyar yau Lahadi.

 

Yace tun zamanin Sarkin Kano na shida a daular Sarakunan fulani Masarautar Jama’are da ta Kano suke da alaka mai karfi a tsakaninsu.

Talla

 

Ya kuma yabawa Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, bisa ziyarar da yakaiwa Marigayi tsohon Sarkin Jama’are dake Jihar Bauchi.

 

Daya ke jawabi, Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero CFR, ya ja hankalin Sabon Sarkin na Jama’are da yaji tsoran Allah yayin da yake gudanar da mulkin sa a masarauta wajen kula da hakkin al’ummar sa.

 

A Cikin sanarwar da sakataren yada labarai na Masarautar kano Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa kadaura24 yace Sarkin ya kuma bukaci sabon sarkin da sanya hakuri a cikin tsarin mulkinsa da kuma janyo “yan uwansa a jiki domin taimaka masa wajan gudanar da mulkinsa.

 

Alhaji Aminu Ado Bayero, ya kuma hori yan’majalisar sabon sarkin su tabbatar sun nuna masa hanya madaidaiciya a cikin shugabancin nasa.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abubakar Bichi ya bada gudumawar motocin bas 13 ga jami’o’in Kano da taraktoci 11 ga yan mazabarsa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu Dan Majalisar tarayya mai wakiltar karamar...

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...