2023: An yiwa Musa Iliyasu Kwankwaso addu’ar samun nasarar zabe a Masarautun karaye

Date:

Daga Nura Abubakar Cele

Mai Martaba Sarkin Karaye Alhaji Ibrahim Abubakar III ya umarci babban limamin Masarautar karaye ya yiwa dan takarar dan majalisar wakilai na kananan hukumomin kura madobi da garun Mallam Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso addu’o’in samun nasarar zaben dan majalisar wakilai.
An gudanar da addu’o’in ne lokacin da musa Iliyasu Kwankwaso ya ziyarci fadar Sarkin domin neman tubarrakin Sarkin kan takarar dan majalisar wakilai da yake yi a jam’iyyar APC.
Musa Iliyasu Kwankwaso bayan ya fito daga fada
Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso wanda shi ne Sarkin yaƙin Masarautar karaye yace ya ziyarci fadar Masarautar ne domin neman Sanya albarka sarkin kasancewar sa uban kasa Kuma Sarkin da karamar hukumar madobi take karkashin Masarautar sa.
Talla
” Babu shakka al’ummar karkara suna Jin dadin wadannan Sabbin Masarautun da gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya farfado da su, wanda hakan yake nuna cewa al’ummar wadannan yankuna ya zasu zabi jam’iyyar APC tun daga sama har kasa, saboda abun alkhairi da akai musu”. Inji Musa Iliyasu
Yace samar da Masarautun sun sa an Sami cigaba mara misaltuwa a kananan hukumomin da wadannan Masarautu suke, ta fuskar aiyukan raya kasa da cigaban al’umma da kuma Kara samar da aikin yi dama matso da mulki kusa da jama’a.
Musa Iliyasu Kwankwaso da yan tawagar sa
” Ina matukar farin ciki bisa yadda al’ummar yankin kura madobi da garun Mallam suka karbi takarar da nake yi, Kuma hakan ya nuna cikin ikon Allah zan lashe zaben, Kuma zamu tafi da kowa zamu taimaki har wadanda ba yan jam’iyyar mu ba, saboda dama halinmu kenan Kuma ba zamu chanza ba”. Inji Kwankwaso
Musa Iliyasu Kwankwaso ya kuma bada tabbacin nan gaba kadan zai ziyarci Masarautar Rano kasancewar kananan hukumomin kura da garun Mallam a karkashin Masarautar suke domin neman Sanya albarka a takarar sa daga mai Martaba sarkin Rano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...