Daga Rukayya Abdullahi Maida
An nada Shahararren malamin addinin musuluncin nan na Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa a matsayin babban limamin masallacin Juma’a wanda Sen. Rabi’u Musa Kwankwaso ya gina.
A cikin wata sanarwa da gidauniyar Kwankwasiyya Development Foundation ta fitar tare da hadin gwiwar Sanusi Bature Dawakin Tofa da Dokta Yusuf Ibrahim Kofar mata, Daurawa, tare da wasu fitattun malaman addinin Islama guda bakwai an sanar da nada su a matsayin Limamai da mambobin kwamitin gudanarwa na Masallacin Juma’ar dake a Miller road, a unguwar Bompai a Nasarawa GRA, Kano.

Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP ne ya gina masallacin a karkashin gidauniyar sa ta agaji mai suna (Kwankwasiyya Development Foundation) kuma ya bayar da gudunmuwar ga jama’a ya ce an yi aikin ne domin ya zama sadakatujjariya ga mahaifinsa marigayi Alh. Musa Kwankwaso, Majidadin Kano wanda ya rasu a ranar 24 ga Disamba, 2020.
Sanarwar ta ci gaba da cewa:
Wadannan sune sunayen jerin limaman Masallacin Juma’a na Alh. Musa Kwankwaso da Kuma bambobin hukumar gudanarwar addinin Musulunci ta Amana Islamic Centre, Kano.
1. Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa (Babban Limami kuma Shugaban Cibiyar).
2. Sheikh Sadiq Isa Abdullahi (Imam)
3. Sheikh Gwani Baffa Ite (Imam).
4. Sheikh Bazallah Nasir Kabara (Imam)
5. Dr. Sani Ashir (Mamban kwamitin).
6. Dr Muhammad Khamis Hussain (Sakatare kuma memba)
7. Sheikh Nura Abdullahi Salihu (Dan Majalisar).
8. Malam Ashir Nata’ala (limamin kamsusalawat).
sanarwar ta bayyana cewa masallacin mai suna Alh. Musa Kwankwaso an kaddamar da shi ne da Sallah juma’a a ranar Juma’a 21 ga Oktoba, 2022 yayin da Amana Islamic Centre za a kammala tare da kaddamar da ita a shekara mai zuwa.