A dena fargaba, mu na da isashshen man fetur a Nigeria – IPMAN

Date:

Daga Ibrahim sani gama

 

Kungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya, IPMAN, a yau Alhamis ta ce kamfanin man fetur na ƙasa, NNPC/Pipelines and Product Marketing Company, PPMC, na da isasshen man fetur a kasa.

 

IPMAN ta ce akwai jiragen ruwa sama da 20 cike da man fetur a kasa suna jira a sallame su a Legas.

Talla

Jami’in hulda da jama’a na IPMAN, PRO, Suleiman Yakubu ne ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ta wayar tarho a Abuja, yayin da yake ƙarin haske a kan matsalar karancin mai da dogayen layukan motoci a gidajen mai da ke Abuja.

 

Yakubu ya ce abin da ya jawo karancin man ambaliyar ruwa me da ya shafi gadar Lokoja wanda hakan ya hana manyan motoci wucewa zuwa wurare daban-daban.

 

Ya ce karancin man fetur din ba wai da gangan ba ne, ibtila’i ne ya haddasa shi, inda ya ce gwamnati na yin duk mai yiwuwa don ganin an shawo kan matsalar.

 

“Ambaliya ta ragu a yanzu kuma motocin suna wucewa sannu a hankali, muna bukatar mu yi haƙuri har sai abin ya daidaita wanda yawanci yakan ɗauki kwanaki kaɗan,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...