Daga Rukayya Abdullahi Maida
Rundunar yan sanda ta jihar Kano ta sanar da samun nasarar cafke barayin motar limamin masallacin juma’a na ITN garin Zaria.
Kakakin hukumar yan sanda na jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ne ya bayyana haka a shafinsa na Facebook, inda yace sun cafke mutane biyu, kuma sun tattara bayanai akansu.
Tunda fari dai wani ne ya ga motar akan titin Dorayi/Panshekara an kai ta wajen kanikawa, bayan sanarwar da ya gani a shafukan sadarwa na zamani, hakan yasa aka sanar da caji ofis din Panshekara, har aka samu nasarar cafke barayin motar.
“MUN KAMA BARAYIN DA SUKA SACE MOTAR MALLAM
Bayan ganin wannan rahoton, mun tattara bayanai, mun samu mota a nan Jihar Kano muna kyautata zaton itace. Mun kamo mutane biyu. Masu motar sai su kira lambar DPO kamar haka; 08039643675”. Inji Kiyawa
