Daga Aisha Abubakar Mai agogo
Wani magidanci mai shekaru 49, mai suna Baba Idi, ya shiga hannun ‘yan sanda a Kano bisa zargin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 3 fyade, Khadija Adamu, aka, Yasmin.
An kama wanda ake zargin ne a ranar 29 ga watan Agustan 2022 biyo bayan karar da mahaifin mamaciyar ya kai wa ‘yan sanda.
A wata hira da ya yi da SAHELIAN TIMES, kawun marigayiyar, Bilyamu Abubkar, ya bayyana cewa mahaifiyarta ta zo yi mata wanka, sai aka ga jini a al’aurar ta.
“Lokacin da mahaifiyarta ta tambaya, Yasmin ta tabbatar da cewa Baba Idi ne yake yi mata wani abu, kuma ya yi mata barazanar cewa zai kashe ta idan ta gaya wa mahaifinta,” in ji shi.
A baya dai baba idi ya taba shigar da marigayiyyar zuwa wani shagon gidansu yarinyar kuma ya yi mata fyade.
Yanzu haka manema labarai sun mallaki rahoton likita wanda ya tabbatar da an yiwa Yasmin fyade.
A cewar kawun, daga baya aka kai Yasmin hedikwatar ‘yan sanda domin tantance wanda ake zargin.
Ya kara da cewa “Lokacin da ta gan shi, sai ta fashe da kuka, tana mai cewa ya yi alkawarin zai kashe ta kuma ya baiwa kuraye ita su cinyeta,” in ji shi.
Khadija ta yi rashin lafiya bata jima ba bayan kwana uku ta mutu tana cewa “shi, wanda ake zargin, “zai kashe ni.”

