Dan Chinan da ya kashe Ummita ya roki kotu ta dage shari’arsa har sai ya samu lauya

Date:

Daga Rahama Umar kwaru

 

Wata Babbar kotun jahar Kano bisa jagorancin mai Shari’a sunusi Ado Ma’aji ta saka ranar 4 ga watan Oktoba 2022 domin sake gurfanar ɗan ƙasar Chaina nan mai suna Geng Quanrong da ake zargin sa da hallaka wata budurwa mai suna Ummukulsum Sani Buhari har cikin gidansu a birnin Kano.

 

A zaman kotun na wannan rana ta Alhamis wanda ake tuhuma Quarong bashi da lauya har ya roƙi kotun data ɗage shari’ar zuwa wata ranar domin ya samu lauya.

 

Lauya gwamnati kuma kwamishinan Shari’a na jahar Kano Barista Musa Abdullahi Lawan bai yi suka ba akan roƙon da Quarong ya yi.

Talla

Zaman na yau bai yiwuba ne sakamakon rashin lauya da wanda ake tuhuma yake da shi , kuma tuhumar da ake yi masa babban laifi ne.

 

Wanda lauyan Gwamnati ya roƙi kotun da ta saka ranar ci gaba da sauraran shari’ar a kusa .

Talla

 

A ƙarshe alƙalin kotun mai Shari’a Sunusi Ma’aji ya ɗage zaman kotun zuwa 4 ga watan Oktoba 2022 domin sake gurfanar da shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...