Amotekun: Buhari ya haramta siyan makamai ga jami’an tsaron sa kai

Date:

Daga Auwal Alhassan kademi

 

Fadar shugabancin kasar Najeriya, ta ce babu wata jihar da aka ba wa izinin siyan makamai masu sarrafa kansu ga jami’an tsaron da ba na gwamnatin tarayya ba.

 

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

 

Ya ce shugaban kasar ya sha bayyana wa karara cewa babu wanda aka yarda ya dauki AK-47 ko wani makami mai sarrafa kansa ba bisa ka’ida ba kuma dole ne ya mika shi ga hukumomin da abun ya shafa.

Kwamishina Noma na Kano ya Baiwa Aliyu Harazimi Rano Gwaggwaban Mukami

 

Gwamna Rotimi Akeredolu na jihar Ondo a ranar 22 ga watan Satumba ya soki gwamnatin tarayya kan cewa tana adawa da shirin amfani da makamai da ake son bawa jami’an sa kai na Amotekun, bayan da ta kyale amfani da makamai a jihar Katsina.

 

Talla

Gwamnan ya bayyana kudurin sa na samar wa Amotekun makamai, domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar yankin.

 

Ya ce matakin, tamkar tauye hakkin Amotekun ne na rike makamai domin kare al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...