Ƴan sanda sun cafke ɗan shekara 84 ya yi wa ƴar shekara 8 fyade

Date:

Daga Rahma umar kwaru

 

Yan sanda a Ogun sun kama wani dattijo mai shekaru 84, Stephen Jack, da laifin yi wa ƴar shekara takwas fyaɗe.

 

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar, Abimbola Oyeyemi, ya bayyana haka a Abeokuta s yau Asabar, inda ya ce wanda ake zargin yana zaune ne a unguwar Okun Owa da ke Ijebu-Ode, kuma ya yi ƙaurin suna a neman ƙananan yara.

 

Talla

Ya ƙara da cewa mahaifin wanda aka kashen ne ya kai rahoton kubucewar Jack ga ‘yan sanda da ya lura cewa ‘yarsa na zubar da jini daga yankinta.

A kullum ana bukatar ruwa sama da Lita miliyan 200 a kano – Kwamishinan ruwa

 

Oyeyemi, Sufeto na ƴan sanda, ya bayyana cewa da aka yi masa tambayoyi, wacce a ka yi wa fyaɗen ta shaida wa mahaifinta cewa Jack ya yi lalata da ita.

2023: NNPP ta ƙaryata cewa ta ajiye Kwankwaso ta ɗau Tinubu a Osun

 

Ya kara da cewa an kai yarinyar zuwa babban asibitin Ijebu-Ode domin yi mata magani.

 

 

Kwamishinan ƴan sanda a jihar, Lanre Bankole, ya kuma bayar da umarnin a kai Jack sashen binciken manyan laifuka domin gudanar da bincike tare da gurfanar da shi gaban kuliya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...