Daga Rahama Umar kwaru
’Yan kasar kasar Lebanon mazauna Kano sun samar da wani asibiti na zamani a babban birnin jihar.
Hakan ta bayyana ne lokacin da Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya kai ziyarar gani da ido ranar Litinin a unguwar Bompai, a cewar Jami’in yada labarai na fadar, Balarabe Kofar Na’isa.
Asibitin na dauke da gadajen kwanciya 25, an kuma samar da na’urori na zamani domin gwaje-gwajen cututtuka, baya ga wurin kabar haihuwa, da kuma kula da jarirai.

Sarkin Kano ya yi murna da samar da asibiti , a matsayin wani babban cigaba da ya zo wa al’ummaar jihar kano baki daya.
Sannan ya ce, asibitin zai rage yawan fita waje da ’yan Najeriya ke yi domin neman magani.
Karanta‘Yan kasuwa a kano sun yabawa Ganduje bisa gyaran wasu titunan jihar
A jawabin shugaban asibitin, Abbas Hajaaj ga sarki a yayin ziyarar, ya ce sun samar da asibitin ne domin kishin jihar, an kuma sa masa suna asibitin ’yan Najeriya da ’yan Lebanon.
Murtala Sule Garo ya Sasanta Rikicin kungiyar APC Media Forum
A cewarsa, nan ba da dadewa ba za a yi bikin kaddamar da shi, bayan kammala daukar sabbin likitoci da ma’aikatan jiyya da na gudanarwa.