Yajin aiki: ASUU ta garzaya kotun ɗaukaka ƙara

Date:

Daga Aliyu Abdullahi Danbala

 

Kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ta garzaya kotun ɗaukaka kara da ke zamanta a Abuja, inda ta bukaci ta yi watsi da hukuncin da kotun masana’antu ta kasa, NIC, ta yanke na janye yajin aikin da ta shafe watanni bakwai tana yi.

 

KarantaBuhari damisar takarda ne kawai – Sen. Rufa’i Hanga

 

Kungiyar, a cikin ƙorafe-ƙorafe 14 da ta shigar, ƙarƙashin tawagar lauyoyinta karkashin jagorancin wani dan rajin kare hakkin bil’adama, Femi Falana, SAN, ta kuma bukaci a dakatar da aiwatar da hukuncin.

 

KarantaKu dakatar da ni idan kun Isa – Wike ya fada wa PDP

 

Idan dai ba a manta ba, a hukuncin da NIC ta yanke a ranar Larabar da ta gabata ta hannun mai shari’a Polycarp Hamman, ta umurci malaman jami’o’in da ke yajin aikin da su koma ajujuwa, har zuwa lokacin da za a yanke hukunci kan karar da gwamnatin tarayya ta shigar domin neman sahihancin yajin aikin na su.

 

Dokar wucin gadi ta umurci mambobin ASUU da su koma bakin aiki, ya biyo bayan bukatar da FG ta shigar ta hannun lauyanta, Mista James Igwe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...