Nafi kowanne dan takarar majalisar tarayya a Nasarawa chanchanta – Aminu Ala

Date:

Daga Abdulhamid Durimin iya
Shahararren mawakin nan Alhaji Aminudden ladan Abubakar wanda aka fi sani da Alan waka, wanda Kuma shi ne dan takarar majalisar tarayya a Nasarawa a jam’iyyar ADP yace duk cikin yar takarar majalisar tarayya a karamar hukumar Nasarawa yafi kowannen su chanchanta .
Aminudden ladan Ala ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da wakilin Kadaura24 a Kano.
Alan waka yace a batun wakilcin al’umma ana bukatar mutumin da yake da yasan matsalolin al’umma Kuma yasan hanyoyin da zai bi wajen magance matsalolin Kuma ni nasani.
” Da kake maganar ana yamutsa hazo saboda Sha’aban Ibrahim Sharada ya bani takarar majalisar tarayya, to kake da shi a Nasarawa wanda ya fini chanchanta, kuma baya bukatar a tallata shi, wanda za’a iya nuna shi a matsayin Dan takara kuma ya chanchanta kamata”.
Talla
” A abatu takarar ana bukatar mutum Mai mutunci, mutum shahararre, mutum mai karrama mutane, ana da bukatar mutumin da shekarunsa suka kai kuma mutum mai Ilimi dai-dai gwargwado, Kuma al’umma suka San shi, to sai ka duba duk cikin Yan takarar da ake da su a Nasarawa waye wanda zai baiwa Sha’aban abun da yake bukata idan ba ni ba”. A cewa Alan waka
Ya ce ya kamata mutane su sani sun dade suna bada gudunmawa a Siyasa ta hanyar wayar da akan mutane su zabi shugabanni da wakilai na gari, don haka yace suka ga dacewar a wannan karon suma su fito su gwada damar da kundin tsarin mulki kasa ya basu da kuma basirar da suke da ita.
Alan waka yace ya yi tanadi na abubuwan da zasu taimaka wajen ciyar da al’ummar Nasarawa gaba fiye da yadda suka Saba gani a baya.
Talla
” Zan bada gudunmawa sosai don bunkasa Ilimi saboda sai da Ilimi mutum zai san waye shi, na yi tanadin bada horo da kuma bada tallafi ga Masu kananan masana’antu da ma wadanda basu da sana’o’in da suke don dogaro da kai da dai sauransu “. A cewar ala
Aminudden ladan Abubakar ya yi fatan al’ummar karamar hukumar Nasarawa da jihar kano baki daya zasu cigaba da mara baya ga Dan takarar gwamna Sha’aban Sharada da sauran yan takarar kujeru daban-daban don Samun nasarar jam’iyyar ADP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...