Gwamnatin Kano ta Karawa Masarautan Kano kudaden gudanarwa

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Majalisar zartarwa ta jihar kano ta Kara kudaden gudanarwa ga masarutun Jihar Kano guda 5 domin cigaba da aiki.

 

Kwamishinan yada labarai na Jihar kwamared Muhammad Garba, ne ya bayyana hakan yau, yayin da yake yiwa Yan manema labarai karin haske kan yadda zaman majalisar zartar wa ta aiwatar a zamanta daya gudana jiya karkashin jagoranci gwamna Abdullahi Ganduje a gidan gwamnatin jaha.

 

‘Yan sanda sun kama guda cikin wadanda ake zargi da kisan dan Kabiru Gaya

Muhammad Garba, yace duba da yawan al’umma da sauran nauye nauyen dake Kan majalisar masarautar Kano gwamnatin ta rubanya alawus din masarautar daga miliyan hamsin zuwa miliyan dari.

  1. ” Su Kuma sauran Masarautun guda hudu wadanda suka haɗa da Bichi, Rano Karaye da Gaya an Kara musu daga Naira Miliyan 20 ya koma Naira Miliyan 40 domin inganta aiyukan su”. Inji kwamishinan

Ban janye daga takarar majalisar tarayyar Gezawa da Gabasawa ba – ‘Yar takarar PDP

Muhammad Garba yace majalisar zartarwar ta amince da fitar da naira miliyan dari Uku da hudu domin biyan alawus na malama dari biyu da tamanin da bakwai na jami’ar Yusuf tama sule.

Talla

 

Ya kara da cewa majalisar ta sahale za’a baiwa jami’ar kimiyya da fasata ta wudil Naira miliyan tamanin da hudu domin biyan alawus na malaman jami’ar.

 

kwamishinan yace gwamnatin ta kafa wani kwamiti, da zai yi duba Kan gine ginen rukunin gidajen Shiekh isiyaka Rabiu dana Shiekh Nasiru kabara dana Shiekh ja’afar domin gano matsalolin da suka hana masu gidajen tarewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...