Tambuwal ya ce bai sauka daga shugabancin ƙungiyar gwamnonin PDP ba

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Aminu Waziri Tambuwal, Gwamnan jihar Sokoto ya musanta cewa ya sauka daga mukaminsa na shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP.

 

Tambuwal dai yayi takarar shugaban kasa a PDP kafin ya janye wa Atiku Abubakar a zaɓen fidda-gwani na jam’iyyar.

 

Ya ƙaryata rahoton wata sanarwar da Darakta-Janar na ƙungiyar, CID Maduabum ya fitar a yau Juma’a.

 

“Ina mai sanar da jama’a da masu ruwa da tsaki a PDP cewa shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP (PDP-GF), Rt Hon Aminu Waziri Tambuwal. Sabanin rahotannin kafafen yada labarai, Aminu Waziri Tambuwal bai ajiye mukaminsa na shugaban kungiyar ba.

 

“Mambobin kungiyar Gwamnonin PDP suna aiki a bayan fage don warware duk wata takaddama da ta shafi jam’iyyar. Za a gudanar da taron ƙungiyar nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...