Zuba shara a magudanan ruwa ne ke kawo ambaliyar ruwa a kano – Dan azumi Gwarzo

Date:

Daga Sani Danbala Gwarzo

 

Sabon kwamishinan kasafi da tsare-tsare na jihar kano Alhaji Ibrahim Dan azumi Gwarzo ya yi kira ga daukacin alumar jahar dasu guji cushe magudanan ruwa, dan kauceawa yawaitar ambaliyar ruwa a jihar kano.

 

Kwamishinan ya bayyana hakan ne a zantawarsa da wakilin Kadaura24 a jihar kano.

Talla

Kwamishinan yace gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin gwamna Abdullahi ganduje na iya kokarinta wajen samar da aiyukan cigaba ga al’umma.

 

” Ba dai-dai ba ne mutane su rika zubar da shara a magudanan ruwa, saboda yin hakan sabawa hankali sannan Kuma zai haifar da matsalolin da zasu cutar da al’umma Masu tarin yawa”. Inji Dan Azumi

Talla

sannan Dan azumi gwarzo ya jajantawa daukacin Yan kasuwar da iftilain ambaliyar ruwan ya shafa, da Kuma mika ta’aziya ga iyalan wadanda suka rasu a rushewar ginin nan mai hawa biyu na kasuwar yan waya dake Kan titin Beirut.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...