Daga Rukayya Abdullahi Maida
Gwamnatin Jigawa ta rufe dukkan makarantu saboda rashin tsaro
A yau Laraba ne dai gwamnatin jihar Jigawa ta bayar da umarnin rufe dukkanin makarantu a faɗin jihar.
Kotu ta yi watsi da ɗauƙaƙa ƙarar da wanda yai waƙar ɓatanci ga Annabi ya shigar a Kano
Kwamishinan ilimi na jihar , Dr. Lawan Yusuf ya tabbatarwa manema labarai hakan a Dutse a yau.
Punch ta rawaito cewa, a cewarsa, matsalar tsaro ce ta sa aka rufe makarantaun.
Ba mu da wata matsala da Malam Shekarau – Kwankwaso
Yusuf ya ce an rufe makarantun ne da safiyar yau Laraba bayan da jihar ta samu rahoton sirri kan yiwuwar kai hare-hare a makarantun a faɗin ƙasar nan musamman a jihohin kan iyaka.
Ya umurci iyayen daliban da ke makarantun sakandaren kwana da su je su dauke ƴaƴansu da gaggawa.