Yadda Sojoji suka kashe kasurgumin Mai garkuwa da mutane da yaransa 17 a kaduna

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta ce ta kashe wani ƙasurgumi kuma jagoran ‘yan fashin daji da ke ayyukansa a Jihar Kaduna mai suna Alhaji Shanono tare da yaransa 17.

BBC Hausa ta rawaito An kashe Shanono ranar Talata yayin da yake shirin gudanar da taro da wasu yaransa a garin Ukambo mai nisan kilomita 131 daga birnin Kaduna, a cewar wata sanarwa daga rundunar.
Daraktan yaɗa labarai na sojan sama, Edward Gabkwet, ya ƙara da cewa dakarun rundunar Operation Whirl Punch ne suka kai harin ta sama bayan tattara bayanan sirri.
A baya-bayan nan, jami’an tsaron Najeriya na kashe jagororin ‘yan fashin da dama, ciki har da Albdulkarim Boss da yaransa 27 da aka kashe a ƙarshen makon da ya gabata.
Kazalika, a ranar Juma’a dakarun sojan ƙasa sun ce sun yi nasarar kama ƙasurguman ‘yan fashin daji bakwai da masu taimaka musu a jihohin Kaduna da Filato da Nasarawa, duka a arewacin ƙasar.
A gefe guda kuma, ‘yan bindigar na ci gaba da kashewa da kuma garkuwa da mazauna ƙauyuka musamman a jihohin arewa maso yamma, inda suke hana manoma zuwa gonaki da kuma saka musu haraji.

Kakakin sojan sama Edward Gabkwet ya ce Babban Hafsan Sojan Sama na Najeriya Air Marshal Oladayo Amao ya je Kaduna a ranar Laraba don duba ayyukan da rundunare ke yi a yaƙi da ‘yan bindiga a arewa maso yamma.

Kuma yayin wannan ziyarar aiki ce kwamandojin rundunoni daban-daban suka bayyana masa nasarar da suke samu.

“Ba zai yiwu mu ajiye makamanmu ba,” kamar yadda Oladayo Amao ya shaida wa kwamandojin.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce: “Bayan bayanan sirri da muka samu ranar 9 ga watan Agusta cewa Alhaji Shanono ya shirya ganawa da mayaƙnsa a ƙauyen Ukambo, rundunar Operation Whirl Punch ta aika jirgi zuwa wurin.

“Daga sama, an hangi ‘yan ta’adda a ƙarƙashin bishiyoyi da ke kan tudu kuma bayan tabbatar da cewa babu gidajen farar hula a wurin, sai aka bai wa dakaru damar kai hari.

“Rahotannin da mazauna yankin suka bayar sun ce an lalata bindiga fiye da 30 da kuma baburan ‘yan bindiga 20, yayin da aka kashe ‘yan fashi kusan 18, ciki har da Alhaji Shanono, sannan wasu suka raunuka.

“Majiyoyi sun kuma ce an ceto mutum aƙalla 26 da ‘yan bindigar suka yi garkuwa da su sakamakon hare-haren.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...